1) Almasihu, hasken duniya, Begen dukan masu rai, Yesu Rasul, Kalmar Allah, Tun fiI azal kai kaɗai. [Kai kaɗai madauwami ne, Kai kaɗai maɗaukaki.] 2x 2) Kai ka ajiye rigar mulki, Ka bar duk don cetonmu. Zafin mutuwa ba ka ƙi ba, Duk ka sha don ƙaunarmu. [Karƃi yabo, karƃi mulki, Naka ne har abada.] 2x 3) Mutuwa ta rasa iko Bisanka, Mai Nasara. Lahira ta buɗe ƙofa, Ka shiga, har ka fita. [An ɗauke ka can a Sama, Aikinka ka gama nan.] 2x 4) Duk jama'a suna jiran Zuwanka, ya Almasihu, Duk Ekklesiya tana zarnan Kewarka, Mai Cetonta. [Zo da sauri, muna bege, Zo, mu dinga ganinka.] 2x 5) Al'ummai, ku kasa kunne, Shi ne Ubangijinku. Ruhun Allah, jawo mutane Zuwa sawun Mai Cetonsu, [Ɗan Maryamu, Tsatson Dawuda, Ibnu Llahi, Ɗan Mutum.] 2xEn medio de este mundo tenebroso เข้าเฝ้าที่พระพักตร์พระเจ้า Он привел меня в дом пира Ich gebe dir mein Herz Sur ton Eglise universelle Qəlbimin padşahısan Trabajad, trabajad, somos siervos Көз алдыңда баары айкын Hän kohta jo saapuvi تەڭىرگە القىش، قۇتقارۇۇچۇعا
Song not available - connect to internet to try again?