1) Babban malami ne ya zo da dare A wurin Yesu don ya tambaye shi Zancen hanyar ceto, har Yesu ya ce, "A haife ka kuma." KORUS Dole a haife ka, a sake haihuwarka, Hakika, mai neman shiga Sama can Dole haihuwa sau biyu. 2) Ku mutane duk, kasa kunne a nan Ga zancen Yesu Ubangijinmu dai, A bin da ya ce ya shafe mu duka, "A haife ku kuma." Korus 3) Idan kana so ka kai wurin Allah, Ka huta a cikin gidan daraja, Idan kana son rai na har abada, A haife ka kuma. Korus 4) "Zancen nan da wuya, ba dama." ka ce Ka zo wurin Yesu, zai yiwu sosai Shi yana da ikon al'ajabi fa, Zai sake haihuwarka. KorusVen Y Subamos A Sion Plesajme radostne, priatelia Díky za Tvůj kříž О говори ко мне Иисус 回想耶稣在世上 САМО ТЕБ Ey Gökler Ey Yer إقترِبـوا إلي Құдай сені жаратты Io sono la via
Song not available - connect to internet to try again?