1) Babban malami ne ya zo da dare A wurin Yesu don ya tambaye shi Zancen hanyar ceto, har Yesu ya ce, "A haife ka kuma." KORUS Dole a haife ka, a sake haihuwarka, Hakika, mai neman shiga Sama can Dole haihuwa sau biyu. 2) Ku mutane duk, kasa kunne a nan Ga zancen Yesu Ubangijinmu dai, A bin da ya ce ya shafe mu duka, "A haife ku kuma." Korus 3) Idan kana so ka kai wurin Allah, Ka huta a cikin gidan daraja, Idan kana son rai na har abada, A haife ka kuma. Korus 4) "Zancen nan da wuya, ba dama." ka ce Ka zo wurin Yesu, zai yiwu sosai Shi yana da ikon al'ajabi fa, Zai sake haihuwarka. KorusНЕКА ЖИВЕЕ РАДОСТТА In Christ Alone Всем сердцем моим всей душой I Am Nothing Ещё не кончен путь تغيرنى أنا ! Qanday ajoyib Xudoning muhabbati ạnạ yswʿ Je t'ai suivi sur le Calvaire Araıly búgin tań atty
Song not available - connect to internet to try again?