1) Da jininsa ya fansa, da ransa ne ya biya Laifofin duk jama'a, bashi mai girma ne. Ya iske mu a jeji, ya kai mu gidansa, Ba bayi nan gaba ba, ƴaƴan sarautarsa. 2) Me ne dalilin wannan aikin al'ajabi? Ya wuce dukan faɗi, ya zarce tunani. Me za mu kai gare shi, shaidar godiyarmu? Bayi ba su da zaƃi, ko da, mu nasa ne. 3) A cikin mulkin Allah, an kafa hidima. Gare mu aka raba abin da za mu iya. Ba domin ikon kanmu ko kuwa da karfi ba, "Da ikon nawa Ruhu," Ubangiji ya ce. 4) Allah Mahaliccinmu, Yesu mai ba da rai, Ruhu mai taimakonmu, uku a cikin ɗaya, Ranmu da aka saya, aikin da mu ke yi, Ruhunmu duk da jiki, karƃa, godiyarmu ne.بتعديني وبتنجيني Veniţi căci vreau a spune بأرفع إسم إلهى Firmes Y Adelante Верный Вождь Спаситель jzʾ 8 yī nián yòu yī nián Tvá, Pane Kriste, věc to jest byk mnṣwr Moon and stars
Song not available - connect to internet to try again?