1) Ku ji muryar annabci kuwa, da Allah ya faɗa. Ishaya ne ya ambata abin al'ajabi. 2) Ga shi an haifi yaro dai, mu aka bai wa Ɗa. Sunansa. kuwa Al'ajabi, kuma Mai Shawara. 3) Allah mai iko duka kuwa, Madauwamin Uba, Sarkin Salama, mulkinsa ba shi da iyaka. 4) A bisa kursiyin Dawuda, da bisa mulkinsa, Zai kafa shi kan shari'a da kuma gaskiya. 5) Wannan, Allah mai runduna da himmarsa zai yi. Maganarsa zai cika ta, alkawari ya yi. 6) Yau cikin birnin Dawuda fa aka haifi Yesu. Mu tafi can sakarkari, sujada za mu yi.항상 진실케 Письмо отцу Môj Boh vďaka tebe dýcham Her Tu Pîroz î Хоҙайым ҡотҡар Un grido Sene Baglanib Огонь в глазах مقوم المنحنين Ты сказал Я слишком молод
Song not available - connect to internet to try again?