1) Makiyaya da daddare sun tsare garkensu Mala'ikan Allah ya zo, ya haskaka su fa. 2) "Kada ku ji tsoro," ya ce, gama sun firgita, "Labarin murna ne na kawo ga dukan duniya". 3) "An haifi Almasihu yau, a birnin Dawuda fa, Mai Ceto, Ubangiji ne, alamarsa ke nan". 4) "Jariri za ku iske ma da siffar mutane A nannaɗe da tsummoki cikin sakarkari." 5) Da gama faɗin saƙon nan, taron haske ya zo, Mala'iku 'na rerawa, suna ta yin yabo. 6) "Ɗaukaka duk ga Allahnmu, salama ga duniya, Aminci ga mutane duk, yanzu da koyaushe."Když Pán tvůj táže se ʿywnnạ bttrjạk tyjy wttnạzl lynạ Můj Spasitel zná cestu Maranata Прощенье мне подарил Господь "SEND THE LIGHT" أما أنا فصلاة - تأمل Ven alma que lloras Go To Dark Gethsemane ʿ ạlḥryẗ
Song not available - connect to internet to try again?