1) Maɗaukakin Sarki madauwami ne, Kai ne kuma mafarin hikima duk. Walƙiyar darajarka ta makanta mu, Mai iko, mai nasara, ya Allahnmu. 2) Mulkinka mai haske ya tabbata nan, A hankali, a natse saukowarsa. Albarkarka tana zubowa kanmu, Alheri mai yawa da nagartarka. 3) Kai ne mai rayad da talikanka duka, Da lafiya da ƙarfi da iyawa kuwa. Mun ga jamalinka cikin halitta, Gwanintar aikinka ka bayyana kuwa. 4) Da rana da wata har taurari kuwa, Kyawawan tafukka, da Kogin Kwara, Da duwatsu duk da tuddai suna yi Wa sunanka yabo, ya Mahalicci. 5) Ya Ubangiji mai girma, Mai Tsarki ne kai; . Allah ne na zurfafa da al'arshi, Mala'ikunka suna yin sujada, Mu fa sai biyayya za mu yi maka.جلس الرب يسوع ماحدش بيحبك أبداً أد الرب يسوع I himlen er det mange ting yạ yswʿ qlbk ḥạny بمراحم الرب أغني كيف أنسى سيدي الغالي ạlrb sạkn jwh qlby Итак расстанемся с тобой Proč bych neměl vesel být ЕТО МОЯ ПСАЛМ
Song not available - connect to internet to try again?