1) Maɗaukakin Sarki madauwami ne, Kai ne kuma mafarin hikima duk. Walƙiyar darajarka ta makanta mu, Mai iko, mai nasara, ya Allahnmu. 2) Mulkinka mai haske ya tabbata nan, A hankali, a natse saukowarsa. Albarkarka tana zubowa kanmu, Alheri mai yawa da nagartarka. 3) Kai ne mai rayad da talikanka duka, Da lafiya da ƙarfi da iyawa kuwa. Mun ga jamalinka cikin halitta, Gwanintar aikinka ka bayyana kuwa. 4) Da rana da wata har taurari kuwa, Kyawawan tafukka, da Kogin Kwara, Da duwatsu duk da tuddai suna yi Wa sunanka yabo, ya Mahalicci. 5) Ya Ubangiji mai girma, Mai Tsarki ne kai; . Allah ne na zurfafa da al'arshi, Mala'ikunka suna yin sujada, Mu fa sai biyayya za mu yi maka.Uram, jövök hozzád Rəbb bizə göndərib nurlu Kəlamlar ṭwby̱ lạ̉nạs Би баярлаж байна رنموا لله أنا ليا إله عينه عليا Джанъм Кьоле Пазарънда ạ̉nạ jyt ʿlsẖạnk Veri Jeesuksen أنا التراب افتكري يا نفسي
Song not available - connect to internet to try again?