1) Na zo gare ka, ya Allahna, Ba ni da kome a hannuna fa. Ga zunubai dayawa ƙwarai, Ya Ubangiji, yi mini jinƙai, Ya Ubangiji, yi mini jinƙai. 2) Yesu ya mutu don laifina, Na sami ceto don alherinsa, Yi mulkin raina, ya Sarkina, Ka tsarkake ni, in bi nufinka, Ka tsarkake ni, in bi nufinka. 3) Zuciya da ruhu, duk naka ne, Na miƙa jikina baiko mai rai. Ba nufin kaina na ke so ba, Sai nufi naka, ya kai Allahna, Sai nufi naka, ya kai Allahna. 4) Inda ka kai ni duka zan bi, Ya Ruhun Allah, Ruhu Mai Tsarki, Ka cika zuciya da ƙaunarka, Har zan yi murna da bin nufinka, Har zan yi murna da bin nufinka:Тебе Господь мой Царь я сердце отдаю ṣwtẗ ạlḥlw Դու Հզոր Ես Սուրբ Ես دي راسي وكتافي بنتغير fy strk tḥt ẓlk كفاية يا نفسي دموع Диңе Худай билен Пасха Бен Гюнахлъ гидеджек йерим йок
Song not available - connect to internet to try again?