1) Sunan wani yaro fa, Daniel ke nan, An haife shi cikin Yahudiya wata ran. Cikin zamaninsa, Allah ne ya sa Mutanensa su horu a ƙasar magauta. KORUS Tsoron Ubangiji farkon ilmi ne, Sai mu tsaya kamar yadda Daniel ya yi. 2) Cikin aikin sarki dai, ya yi aminci. Aka gabatad da shi ya zama sananne. Cikin wannan duka, shaida ya ke yi, Ba ya neman girman kansa, sai na Allahnsa. Korus 3) Zancen yin addu'arsa, ba ya fasawa, Kunya ba ya taƃa ji a cikin wannan ba. Can fa wata ra na a ke ƙararsa, Duk da haka ya yi ta addu'a kamar da. Korus 4) Cikin ramin zakuna aka jefa shi, Ba su iya buɗe baki ba, balle su ci. Daniel ya kwana lafiya ƙalau, Can da safe ya ji muryar sarki, cewa "Zo" Korus 5) Ikon Ubangijinmu ba ya kasawa. Har yanzu akwai shi isasshe ne dominka Kada ka yi shakka, ko ka ji tsoro Wurin Ubangiji dukan kome ya yiwu.موسيقى rby ạ̹ny lk Isus va cheama auziţi Paś owieczki Me Dans le lieu saint Grande Gozo Hay En Mi Alma Ži vo mne, drahý Kriste Bila 'Ku Tertidur Over Kidron Jesus Treadeth Eu ma culc, sunt obosit
Song not available - connect to internet to try again?