1) Wa ke samun albarka daga Ubangiji ? Wanda ya ke karanta Daga Litaffinsa. Har ya ji ya kiyaye Abin da ke ciki, Shi zai sami albarka Daga hannuwansa. 2) Wa ke samu albarka daga Ubangiji ? Wanda an gafarta Masa duk laifofinsa Ba lissafta gare Dukan muguntarsa. Allah zaya zubda su Cikin zurfin teku. 3) Wa ke samu alabarka daga Ubangiji ? Wanda ba ya biba ta Shawarar mugu ba. Ko a cikin hanyarsa Ba ya tsaya a ciki, Marmari da tunani Cikin shari'arsa. 4) Wa ke samu albarka daga Ubangiji ? Shi mai faɗin gaskiya Cikin zuciyarsa. Yana tafiya sosai Da aikin adalci Ba shi tsegume daɗai Ko zagin abokan shi. 5) Wa ke samu albarka daga Ubangiji ? Wanda a ke tsananta Sabo da adalci Ko mu kan sha wahala Sabo da sunansa Ladarmu mai girma ce Can a cikin sama. 6) Wa ke samu albarka daga Ubangiji ? Wanda ya ke jimrewa Lokacin jaraba Allah Mai aminci ne Ya yi hanya tsira Farin ciki mu ke yi Don ya ci nasara. 7) Wa ke samu albarka daga Ubangiji? Wanda ya ke jiransa Komowar ɗan Allah. Ya yi shirin zamansa, Ya bar bin duniya. Yesu yana zuwa kuwa Biɗan masu-binsa.Tak Mudah Jalanku مهر تو هر دم شود افزون حضرت مسیح عیسی غاليين عليك dwsy yạ nfsy Atyń dańqtalsyn ạ̹nt srwry كەچۈرگىن خۇدا มีของบางสิ่งที่ฉันไม่รู้ نادم على كل ثانيه Seniń mahabbatyń jarqyrap tur
Song not available - connect to internet to try again?