1) Ya ku zukatan mutane, Rashin sani kuka yi, Kamar ƃatattun tumaki, Wurin kiwo ku ke ki. 2) Ko kun san wani kamarsa? Almasihu ya fi duk Ƙauna, taimako, har kuma Ceto daga zunubi. 3) Ya ku zukatan mutane, Shakka ce ta hana ku? Sai ku dogara gare shi Wanda ya ke ƙaunarmu. 4) Sai ku zo, ku ji, ku gwada, Yesu mai aminci ne. Maimakonmu shi ya cika Nufin Ubanmu daidai. 5) Cikin Yesu mu ke samun Sanin Allah, sanin rai. Kuma aka ɗora masa Duk alhakin zunubai. 6) Da kun gaskata maganar, Da ya sake halinku, Da ya sabonta zukata, Da ya zauna cikinku. 7) Ƴanuwa, mu yi godiya, Sai mu ƙaunace shi dai. Ba dalilin tsoro kuma Har iyakar zamanai.Джанъм Рабби Гьозлюйор mzmwr 117 - mrnm Világosságod küldd el ạ̹dạny ḥyạẗ Dame, Te Ruego Iso hayot, Iso sevgi مەن سىلەر بىلەن ھەمىشە تۇراي بعد ما كنت عبد أسير Приблизь меня к Себе 在谷中我遇见你
Song not available - connect to internet to try again?