1) Ya Ubangijinmu, Kalmarka ta dauwama Wajib ne a gaskata, a kuma karƃe ta. 2) Idan maƙiyanmu suna tsananta mana, Maganar cetonka ita ce ƙarfinmu. 3) In wahala ta zo, ko masifa ta taso, Haskenka zai bishe mu, za ya kiyaye mu. 4) Wa ya san misalin murna mafificiya Ta miƙa bishararka zuwa mutanenka. 5) Jinƙanka ke ba da taimako ga masu rai, Maganarka ta'aziyya ga wanda ke mutuwa. 6) Mu da muka gane tsarkin wannan Kalma, Sai mu ƙaunace ka, don kullum mu bi ka.ادامدار اداسار Құрбан еттің біз үшін Mon Dieu pourvoira à tous vos besoins Я хвалюсь Христом Если ты устал идти 有一句话我们永远要说 يا ملك الملوك Kruitjie-roer-my-nie Così come sei bʿd sjwdy
Song not available - connect to internet to try again?