1) Ya Ubanmu, sa albarka Bisa kan ƴaƴanka yau. Za mu yi yabon sunanka, Addu'a kuma za mu yi. Mun ji labarin Ubangiji Na gaskiya da alheri. Cikin hasken Almasihu Za mu gane ƙaunarka. 2) Maganarka ta koya mana Mu ƙaunaci ƴanuwa, Mu girmama gaskiyarka, Mu yi haƙuri kullum, Mu hori kanmu da aniya Domin mu yi aikin kirki, Loton shiru ko na faɗi, Koyaushe sai kamewa. 3) Bari ruhohinmu duka Su yi yabon ikonka. Murna, ƙauna da salama Su kasance wurinmu duk. Mu zama amintattu naka, Ko cikin aiki ko tunani. Tsakaninmu da ƴanuwanmu, Mu yi duk domin Yesu. 4) Mu ɗaukaka sunan Allah, Mu ambaci duk tsarkinsa. Albarka kuwa ga Almasihu Da Ruhunsa Mai Tsarki. Ga Allah Uba, Allah Ɗa kuwa, Allah Ruhu Mai Tsarki, Mu ha ka dukan daraja ma, Allahnmu har abada.mḥkmẗ ạlʿdl ạlsmạwyẗ Пролей Свой дождь จงยอพระเกียรติพระเจ้า Jak jeleň dychtí za vodou Only a sinner saved by grace Ka Ngaklah Tai rgẖm ạlḍyqẗ Lay ora tao Getsemane Ekmeyim suyum sensin بيكي أمجاد يا مدينة الله
Song not available - connect to internet to try again?