1) Yau an haifi Almasihu, Ɗan Maɗaukaki ya zo, Yau Immanuel ya samu zamansa a wurinmu. Allah ne ya isa duniya, Kalma tasa nan ya sauko, Cikin jiki rufaffe, amma Ubangiji ne, Cikin jiki rufaffe, amma Ubangiji ne. 2) Budurwa ta haifi Ɗanta, shi ne Ɗan Mai Tsarki. Jibra'ilu ne ya shaida sunansa Mai Ceto ne. Ɗan Adam ne aka haifa, muna yi masa sujada. Girma fa da ɗaukaka, nasa ne har abada Girma fa da ɗaukaka, nasa ne har abada. 3) Haihuwarsa al'ajibi ce, ƙauna ba ta aunuwa, Har ya ajiye duk sarauta, har ya shiga mutuwa. Zo, mu gai da Almasihu, mu da Allah muka sadu. Yesu haihuwar budurwa, Allah ne mai girma, Yesu haihuwar budurwa, Allah ne mai girma.Sen Yücesin Rab Là où tu iras Det Blod som Jesus gav for meg lsh ạlạml mwjwd Senin gibi görebilmeyi Баҳ! - фарёд омад Ümidini itirmə sən, gəl Allahın hüzuruna ạ̉nt wḥdk ạlạ̹lh Boh je medzi nami mḥtạj lk yạ yswʿ
Song not available - connect to internet to try again?