1) Yau an haifi Almasihu, Ɗan Maɗaukaki ya zo, Yau Immanuel ya samu zamansa a wurinmu. Allah ne ya isa duniya, Kalma tasa nan ya sauko, Cikin jiki rufaffe, amma Ubangiji ne, Cikin jiki rufaffe, amma Ubangiji ne. 2) Budurwa ta haifi Ɗanta, shi ne Ɗan Mai Tsarki. Jibra'ilu ne ya shaida sunansa Mai Ceto ne. Ɗan Adam ne aka haifa, muna yi masa sujada. Girma fa da ɗaukaka, nasa ne har abada Girma fa da ɗaukaka, nasa ne har abada. 3) Haihuwarsa al'ajibi ce, ƙauna ba ta aunuwa, Har ya ajiye duk sarauta, har ya shiga mutuwa. Zo, mu gai da Almasihu, mu da Allah muka sadu. Yesu haihuwar budurwa, Allah ne mai girma, Yesu haihuwar budurwa, Allah ne mai girma.Chisʋs pi Okchalinchi, pi̱ Mi̱ko ma! İsminde ne güzellik var غربتنا يا رب طالت Oh das Blut Jesu Sənə alqışlar olsun, Səninlə şadlanıram Аллилуйя 他在全地被尊崇 I heard a voice Божия звезда كنت في طين الحمأة
Song not available - connect to internet to try again?