1) Yesu mu ne naka, kai ka saye mu, Ga kuwa muna zuwa bayanka yanzu. Inda za ka duka, wurin za mu bi, Kome wuyar aiki, lalle za mu yi. Kome ya same mu, ko a cikin rai, Ko ya kai ga mutuwa, Yesu mu ke bi. 2) Masu Bi, ku tashi, yi da zuciyarku, Aikin Ubangiji yana jiranku. Ga mutanen duniya, duhu su ke bi, Ba sa bin tafarki, ƙaƙa za mu yi ? Lalle sai mu tashi, hutu sai mu ƙi, Har labarin Yesu dukansu sun ji. 3) Duba can a Sama, ga mazuninmu, Daraja da tsarki, ba misalinsu. Babu saura kewa, babu rabuwa, Babu sauran cuta, babu mutuwa. Gaba dai, ƴanuwanmu, yad da duniya, Sama mu k enema, gidan tsarkaka. 4) Kome daɗin Sama, wanna ne mai fi, Yesu za mu gani, Yesu za mu ji. Ƙafa, hannu, goshi, shaida su ke yi Da azabar kansa fansarmu ya yi. Sauri fa, jama'a, babu hutawa! Yesu mu ke nema, za mu wurinsa.كللت السنة بجودك - صفوت داود Мой Бог İsa Çocukları Çağırır Si tu a Tvoja sláva نقدم ليك كل السجود Bir kezde senderdi tańdady Táńirim Бак бу дюня, не дюня قينالعان شاقتاردا كۇنالاردان Қудайдың үйи Сказал Господь мне очень тихо
Song not available - connect to internet to try again?