1) Yesu Ubangijinmu, ga mu nan a gabanka. Kai ka kawo dukanmu yinin nan da lafiya Muna rera waƙarmu, muna maka godiya. 2) In yau wata jaraba za ta kai mu haɗari, Ba mu ikon jurewa, ƙara mana ƙarfi kuwa, Kiyaye mu lafiya, har mu ka da zunubi. 3) Bisa ga maganarka, daidaita rayukanmu, Bishe mu da Ruhunka, amshi mulkin nufinmu. Bar mu miƙa gare ka hadaya ta zuciyarmu. 4) Ji yanzu addu'armu, ji mu, muna roƙonka. Da mu duk da ƴanuwa, baiwarka mafificiya Ita ce bukatarmu, sahihiyar zuciya. 5) Haka za mu bayyana yau da gobe godiyarmu. Haka za mu ɗaukaka sunan Ubangijinmu. Za mu shaida yabonka, Almasihu Allahnmu.มีองค์พระคริสต์ข้างกาย ในหัวใจฉัน Lord be Glorified نشكر كل حين إلهنا الأمين تەك ماسىحتە ۇمىتتەنەم أنا محتاج إنك تجذبني Ерөөлтэй тэр өдөр Вещает небо Предвечного славу مەسىھ ئەيسا قۇدرەتلىك hl ạ̉ntm ạldẖy bqwẗ ạllh يا كنيسة يا شعب اللي فداكي
Song not available - connect to internet to try again?