1) Yesu Ubangijinmu, ga mu nan a gabanka. Kai ka kawo dukanmu yinin nan da lafiya Muna rera waƙarmu, muna maka godiya. 2) In yau wata jaraba za ta kai mu haɗari, Ba mu ikon jurewa, ƙara mana ƙarfi kuwa, Kiyaye mu lafiya, har mu ka da zunubi. 3) Bisa ga maganarka, daidaita rayukanmu, Bishe mu da Ruhunka, amshi mulkin nufinmu. Bar mu miƙa gare ka hadaya ta zuciyarmu. 4) Ji yanzu addu'armu, ji mu, muna roƙonka. Da mu duk da ƴanuwa, baiwarka mafificiya Ita ce bukatarmu, sahihiyar zuciya. 5) Haka za mu bayyana yau da gobe godiyarmu. Haka za mu ɗaukaka sunan Ubangijinmu. Za mu shaida yabonka, Almasihu Allahnmu.Kto ze łzami sieje Jesús me pastorea Herr deine Güte reicht so weit bạ̹ymạn wrjạʾ Večerní З ранку і да вечара دْبِژْن بقوة لاسم يسوع kl ạlmkẖạwf MI KIP CA BAIBAL THIANG
Song not available - connect to internet to try again?