1) Yesu Ubangijinmu, ga mu nan a gabanka. Kai ka kawo dukanmu yinin nan da lafiya Muna rera waƙarmu, muna maka godiya. 2) In yau wata jaraba za ta kai mu haɗari, Ba mu ikon jurewa, ƙara mana ƙarfi kuwa, Kiyaye mu lafiya, har mu ka da zunubi. 3) Bisa ga maganarka, daidaita rayukanmu, Bishe mu da Ruhunka, amshi mulkin nufinmu. Bar mu miƙa gare ka hadaya ta zuciyarmu. 4) Ji yanzu addu'armu, ji mu, muna roƙonka. Da mu duk da ƴanuwa, baiwarka mafificiya Ita ce bukatarmu, sahihiyar zuciya. 5) Haka za mu bayyana yau da gobe godiyarmu. Haka za mu ɗaukaka sunan Ubangijinmu. Za mu shaida yabonka, Almasihu Allahnmu.Canta striga bate din palme ஆழமான ஆழியிலும் ஆழமான அன்பு يايسوع نيرك هين Alzo gli occhi al cielo Рəбб Иса, Сəни чағырырам мəн Bože, jenž si v nebesích Всё могу в Укрепляющем меня Можете ли вы ИИСУС - СЕН МЕНИҤ СӰӰЖИМ Unknown
Song not available - connect to internet to try again?