1) Yesu Yana jin addu'a, Yesu Ubangijinmu, Masu sonsa, masu binsa, Su ne nasa cetattu. Yawan sonsu a wurinsa! Su ne tasa dukiya, Yana zuba musu ido, Yana ba su daraja. 2) Yesu yana yin addu'a, Aikin ceto nasa ne, Masu roƙo wurin Allah Sai a cikin sunansa. Shi jagora ne gare mu, Ganin Allah sai da shi, Yesu, shugaban sujadar Da mutane za su yi. 3) Mu ma sai mu yi addu'a, Almasihu yana nan. Kalma tasa ta tabbata, Shi zai yarda da roƙon. Ya riga ya yi alheri, Ya yi mana gafara. Kyautarsa ta wadace mu Har iyakar duniya. 4) Yesun nan, mai yin addu'a, Allah ne ya ɗaukaka. Kada kowa fa ya raina Wanda shi ya girmama. Wata rana in ya komo, Gani kuwa zai kori ji, Tuba dai, ka karƃi ceto Tun da sauran zarafi.Proč bych neměl ạ̉nạ ạ̹nạʾ Ayt hamdu sano Xudoga ترنيمة جديدة وتركت عمري يمضي Бор Бўлган ИСУСЕ, ТИ СИ МОЙ БОГ Бог тебя так любит Հայաստան Ունես կարիքը Քրիստոսի Öveceğim Sonsuzca
Song not available - connect to internet to try again?