1) Ku ta da zuciyarku, kada ta ƃaci kuwa, Ƴanuwan ba su mutu ba, su barci su ke yi. An shirya zamansu a gidan Sama can, Allahnmu ne ya kira su su fita duniyan nan. 2) Ba sauran zunubi, jaraba ba ta can, Wahala duk da ƃacin rai ba za su shiga ba. Su, Yesu su ke bi da muryar nasara, Sunansa yana goshinsu, sun duba fuskarsa. 3) Mun ajiye jikinsu can cikin kabari Har ran da za a ta da su marasa ruƃewa. Shi Yesu Fansarmu, shi ne mai ba da rai, A cikin rashin ruƃa dai, shi za ya ta da su. 4) Mun gode, Allahnmu, domin bangaskiyarsu, Don shaidarsu a wurinmu, kwatancin halinka. Ya Ubangijinmu, ka ƙarfafa mu yau Domin mu bi sawunsu har mu gama aikinmu.Panpih Ka Ngai Ui Álemime tań bolyp atqan Cate daruri minunate Cuando Cristo Vino Komm' Geist des Vaters Isa Ýeňiji God of Revival He Poured In the Oil and the Wine من أنا لأصير qd wqft fy ạ̉bwạb
Song not available - connect to internet to try again?