1) Ku ta da zuciyarku, kada ta ƃaci kuwa, Ƴanuwan ba su mutu ba, su barci su ke yi. An shirya zamansu a gidan Sama can, Allahnmu ne ya kira su su fita duniyan nan. 2) Ba sauran zunubi, jaraba ba ta can, Wahala duk da ƃacin rai ba za su shiga ba. Su, Yesu su ke bi da muryar nasara, Sunansa yana goshinsu, sun duba fuskarsa. 3) Mun ajiye jikinsu can cikin kabari Har ran da za a ta da su marasa ruƃewa. Shi Yesu Fansarmu, shi ne mai ba da rai, A cikin rashin ruƃa dai, shi za ya ta da su. 4) Mun gode, Allahnmu, domin bangaskiyarsu, Don shaidarsu a wurinmu, kwatancin halinka. Ya Ubangijinmu, ka ƙarfafa mu yau Domin mu bi sawunsu har mu gama aikinmu.رضى بي وحن علي Track 12 Басит Այդ Սերն է TU HNUAH KAN I TONG LAI 在我的身边有一个篱笆 Бүргэд Yesu Kristi Ubanjinmu Muna Kawo Maka Godiya Pe malurile râurile triste tậml 1
Song not available - connect to internet to try again?