1)Ku yi ta wa'azi wurin mutane duk, Gama a duniya akwai wahalar rai. Bari duk Masu Bi su shaida ko'ina, Mai Taimako ya zo. KORUS Mai Taimako ya zo, Mai Taimako ya zo, Ruhu Mai Tsarki da Allah ya aiko. Ku labartad da shi wurin mutane duk, Mai Taimako ya zo. 2) Mun sami haskensa, ya watsa duhunmu, Ya kau da tsoro duk, ya ba mu kwanciyar rai. Ya kawo gafara ta dukan zunubi, Mai Taimako ya zo. Korus 3) Ga Ubangijinmu, ya zo da warkarwa. Ga ƴaƴan duniya, ruɗaɗɗu na Shaiɗan. Ya kwance ɗaurarru, ya kawo fansarsu, Mai Taimako ya zo. Korus 4) Ya Allah mai ƙauna, ko ni na iya ƙi In shaida j inƙanka ga dukan mutane? Ga ni da, matacce, ka ba ni sabon rai, Mai Taimako ya zo. KorusRisorto sei ạlʿạlm ybny wyzrʿ Арслан Duch a nevěsta Возвожу мои очи к горам Daniele Jezus Królem naszym jest Ya se fue, ya se fue Après la nuit vient l'aurore Seny alǵıslap qosıq aytaman
Song not available - connect to internet to try again?