1) Mu yi sujada ga Ubangiji, Mu yi godiya domin ƙaunarsa. Da zuciya ɗaya mu ɗaukaka shi, Mu yabi sunansa da duk ladabi. 2) Mu yi tunani a kan girmansa, Mu yi waƙoƙi kan alherinsa, Mai Tsarki, Mai Ƙauna, Mai Gaskiya ne, Mai ikon halitta, mai jin addu'a. 3) Bukatarmu duk shi ya ke ta biya, Mu karƃe su fa tare da godiya. Abinci, abin sha, numfashi da rai, Lissafin kyautansa ya fi ƙarfinmu. 4) Mu raunana ne, amma cetattu, Mu ƴaƴansa ne, bai yashe mu ba. Yana marmari dai mu yi zumunta, Jiƙansa mai yawa, ba misalinsa. 5) Al'amuranmu su girmama shi, Da bakunanmu mu yi ta shaida. Mu bauta masa, mu ji tsoronsa kuwa, Gama shi ne Allah na duk duniya.twklnạ ʿly̱ ạllh Mən tamam itmişdim, Sən məni tapdın Quiero llenar tu trono de alabanza Z Panem umierać Хочу я быть подобным Vyvýšený jsi Pán ạldmwʿ ạlmrẗ sạlt Marhamatlisi Patshanıń balasıman Iza moa io Zazakely
Song not available - connect to internet to try again?