1) Mu yi sujada ga Ubangiji, Mu yi godiya domin ƙaunarsa. Da zuciya ɗaya mu ɗaukaka shi, Mu yabi sunansa da duk ladabi. 2) Mu yi tunani a kan girmansa, Mu yi waƙoƙi kan alherinsa, Mai Tsarki, Mai Ƙauna, Mai Gaskiya ne, Mai ikon halitta, mai jin addu'a. 3) Bukatarmu duk shi ya ke ta biya, Mu karƃe su fa tare da godiya. Abinci, abin sha, numfashi da rai, Lissafin kyautansa ya fi ƙarfinmu. 4) Mu raunana ne, amma cetattu, Mu ƴaƴansa ne, bai yashe mu ba. Yana marmari dai mu yi zumunta, Jiƙansa mai yawa, ba misalinsa. 5) Al'amuranmu su girmama shi, Da bakunanmu mu yi ta shaida. Mu bauta masa, mu ji tsoronsa kuwa, Gama shi ne Allah na duk duniya.ạ̉dnw ạ̹lyk ạ̉rtạḥ ما يحسن في عينيك dy ḥyạẗ jdydẗ Niech Ci błogosławi Pan Я жду Динле Ей Исраил mqbwl ạ̉nạ fy dm ạlmsyḥ Господи في عيد ميلادك يا ربي الملك В тихите среднощни стражи
Song not available - connect to internet to try again?