1) Ya Allah, miƙa hannunka, ka tsai da haukansu, An kashe Almasihunka ta hannun miyagu. 2) Ba za ka bar Mai Tsarkinka cikin kabari ba. Ba za ka bar maƙiyansa su ci nasara ba. 3) Dā, kayayuwa tsinana sun soki goshinsa. Yanzu ka naɗa Almasihu a hannun damanka. 4) Shi wanda aka kunyata a cikin duniyan nan, Ka tashe shi da daraja, ka ba shi girma can. 5) Shi ne ya mutu dominmu, ya ɗauki giciyensa. Mun sami rai da lafiya ta wurin dūkansa. 6) Idan mun mutu tare nan, mun ɗauki giciyensa, Tare kuwa za mu yi murna a cikin mulkinsa. 7) Ina misalin yabonka, ya Yesu Almasihu? An sanya mulkin kome nan ƙarƙashin sawunka.Mes mots sont peu de chose Oui, Dieu règne أمام عرشك أتينا Nang Lam Ka Hun Nga Tai พระเจ้านั้นทรงสร้างเยรูซาเล็ม Dillo forte Adorons le Seigneur A venit de mult de sus Büyük Ve Yücedir, İşlerin Senin دم يسوع يحيط بي
Song not available - connect to internet to try again?