(Kira da Amsa) K : Yesu, Ɗan Allah, Mai Iko duka ne, A : Yesu shi sarki ne, Sarkin Sarakuna. K : Ya bar sarauta a can cikin sama, A: Ya zo a duniya a cikin talauci, K: Ya sha wahala a gun Yahudawa A: Har suka yi shawara, suka giciye shi. K: Ya yi mutuwa fa, mutuwa ta giciye, A: Ya zubda jinisa domina ya panshe mu. K: Bayan kwana uku sai Yesu ya tashi. A: Yesu ya ci nasara, nasara ta mutuwa. K : Ku fa mutane, ku zo fa mu tuba, A : Mu bi Yesu Mai Nasara da mutuwa. K : Sai fa, mu bi Shi da zuciya ɗaya A : Gama babu ceto sai wurin Yesu fa. K: Ku zo maza mutane ku zo maza mu tuba A: Yesu ya hau sama yana shirya wuri. K: Za ya sake zuwa domin masu-binsa. A: Lalle akwai murna ran da mun kai sama. K: Yesu mun gode domin mutuwarka. A: Yesu mun gode domin kai, ka tashi. K: Karɓi sarauta da iko da girma. A: Taka ce har abada, har abada abadin.Nunca Dios mío cesará mi labio Наш Бог велик كم يلذ لي Istotu vzácnu Отче, послушай нас أنا جيت علشانك إنت علمني أكون Az Isten jósága Amado Salvador Все моё сердце Хвалу Тебе поет
Song not available - connect to internet to try again?