(Kira da Amsa) K : Yesu, Ɗan Allah, Mai Iko duka ne, A : Yesu shi sarki ne, Sarkin Sarakuna. K : Ya bar sarauta a can cikin sama, A: Ya zo a duniya a cikin talauci, K: Ya sha wahala a gun Yahudawa A: Har suka yi shawara, suka giciye shi. K: Ya yi mutuwa fa, mutuwa ta giciye, A: Ya zubda jinisa domina ya panshe mu. K: Bayan kwana uku sai Yesu ya tashi. A: Yesu ya ci nasara, nasara ta mutuwa. K : Ku fa mutane, ku zo fa mu tuba, A : Mu bi Yesu Mai Nasara da mutuwa. K : Sai fa, mu bi Shi da zuciya ɗaya A : Gama babu ceto sai wurin Yesu fa. K: Ku zo maza mutane ku zo maza mu tuba A: Yesu ya hau sama yana shirya wuri. K: Za ya sake zuwa domin masu-binsa. A: Lalle akwai murna ran da mun kai sama. K: Yesu mun gode domin mutuwarka. A: Yesu mun gode domin kai, ka tashi. K: Karɓi sarauta da iko da girma. A: Taka ce har abada, har abada abadin.Hayotim Kalom Jeśli z Panem na ziemi tu kroczę องค์พระเจ้าผู้สร้างฟ้าสวรรค์ أنا عايزك إنت Shukrona Fuerzas das al que espera ạ̹lh ạlḥb njạny Its glory just to walk XƏYALIM DOLANIR فاقت أمانة ربي
Song not available - connect to internet to try again?