1) Yesu Ɗan Allah ne, Mai Ceton duniya, Ya ƙaunace mu har ga mutuwa. Wanda ya ba da gaskiya gare shi Lalle ya tsira daga shari'a. KORUS Yesu mai iko duka ne, Ba za ya kasa ba daɗai, Sai mu kai bishara ko'ina a duniya Shi kuwa za ya taimake mu. 2) Ƴanuwanmu sun ƃata cikin duhu, Ba su da rai, ko sanin hanyarsa. Kada su mutu cikin zunubansu, Sai dai su zo su sami gafara. Korus 3) Ubangijinmu za ya sake zuwa Domin ya kai mu can a gidansa. Me za mu ce idan mun ƙi biyayya? Me za mu amsa masa ranan nan? Korus 4) Sauri, jama'a, Yesu yana kiran Duk Masu Bi su kama aikinsa. Maza da mata duk da yara kuma, Tashi, mu yi biyayya nandanan. Korusswf ạ̉nsy̱ ạlạ̉ms dʿwạ ạlạ̉wlạd yạ̉twn ạ̹ly̱ Ózen joldan alshaq emes Кто подобен Тебе yạ yswʿ yạ gẖạly Damai Sejahtera Allah bạsmk yạrb lnạ Xudovandim oldida Tinch Turar Քո Մեծությունը Ti prego salvami
Song not available - connect to internet to try again?