1) Yesu ya kira almajiransa sha biyu. Lokacin da yake komawa sama Ya ce, "Su tafi su yi bishara Har duniya duka ta sami ceto." KORUS Bishara Yesu Za mu yi, za mu yi Babu tsoro fargaba ba za mu yi ba. 2) Sai ku fara a cikin Urushalima, Har in aiko maku da mai taimako. Ruhu mai tsarkina za ya bida ku, Ga shi ina tare da ku a kulluyaumi. Korus 3) Sai ku fara daga Urushalima, Samariya har da Galili. Dukan ƙauyuka suna bukatar ceto. Sa'an nan har iyakar duniya. Korus 4) Ku ɗauki giciyen Yesu domin bishara, Gama duniya tana mutuwa. Idan mu kyale su za su hallaka, Alhakinsu yana rataye a wuyanmu. Korus 5) Wanda ya nace cikin aikin bishara. Za ya sami ladan aikinsa. Za ya sami rawani na rai, Za mu yi mulki tare da shi har abada. KorusΠοιητή και Βασιλιά μου In The Cold Night THLACAM CAAN DAIHNAK A SI Я не оставлю вас одних Когда же Я уйду Your love is higher باشكرك يا يسوع Kde se dva neb tři Più in alto Jeesuksen tähden nouskaa Qudaıdyń Rýhynda kóktegi Ákemmen
Song not available - connect to internet to try again?