1) Yesu Ubangijinmu ne, Jininsa ya saye mu, Daga hannunsa mun sami Ceto daga zunubi. Mu bayinsa, mu bayinsa, Sai mu yi ta aikinsa. 2) Almasihu ya fanshe mu, Ba da azurfa ba fa, Ba kuwa da zinariya ba, Sai da jininsa kaɗai. Mu bayinsa, mu bayinsa, Mu, hakika, nasa ne. 3) Ranmu duka ne ya saya, Rabin zuciya ba ya so. Shi ya ba da ransa duka, Namu duka ya ke so. Mu bayinsa, mu bayinsa, Kome namu za mu bayar. 4) Ga mutane cikin duniya, Ba su san Mai Ceto ba. Shi kuwa yana so su san shi Sai mu je mu neme su. Mu bayinsa, mu bayinsa, Sai mu je mu neme su. 5) Ƴanuwana, sai mu tuba, Sai mu yad da ƙyuyarmu, Ga mutane suna mutuwa, Sai mu ceci waɗansu Mu bayinsa, mu bayinsa, Ƙaƙa za mu ƙyale su? 6) Su da suka yi aniya, Masu yi da zuciya ɗaya, Ran da Yesu za ya komo, Za a ɗaukaka su dai. Bayin Yesu, bayin Yesu, Za su sami ladansu.Görkemli Bir Irmak Tanrı Huzuru Ya Yesu, Ban da Kai, Ban Iya Kome Ba Grande come te Lungo il cammino Seni olqishlayman Nech je zjavená moc Un călător se cobora ถึงเราจะเป็นคนบาปนักหนา Hän kohta jo saapuvi عايز منك هدية 2
Song not available - connect to internet to try again?